TASKAR KASAR HAUSA

JARIDAR GASKIYA TAFI KWABO

JARIDAR GASKIYA TAFI KWABO

Muhimman bayanai guda sha biyu (12) game da GASKIYA TAFI KWABO.

1. Ita ce jaridar Hausa ta farko a Najeriya.

2. An kirkire ta a shekarar 1939.

3. Ita ce jaridar hausa mafi sanuwa a yammacin Afirka.

4. Ita ce jaridar Hausa ta farko a duniya.

5. Ana buga ta sau uku (3) a sati. Tana fitowa sau uku a sati.

6. Jaridar mallakin gwamnonin arewa a karkashin kamfanin Gaskiya Corporation.

7. Ita ce Jarida ta farko mallakin gwamnati a Najeriya.

8. Ta shahara wurin kawo rahotanni Yakin Duniya Na Biyu II.

9. Babban hedkwatan ta a Zariya.

10. Ita ce jaridar cikin gida mafi jimawa a Najeriya, ta dauki tsawon shekaru saba'in tana aiki.

11. Tana bada gudunmawa wajen gwagwarmayar yada kishin kasa da harshen Hausa.

12. Marubuci Dokta Abubakar Imam ne Editan ta na farko